23 Mayu 2020 - 06:36
Keta Alframar Masallaci A Faransa

Masu adawa da muslunci a kasar Faransa sun yi rubutu na barazanar kisan musulmi a kan bangayen masallaci a Cholet.

(ABNA24.com) Shafin yada labarai na sabah yaum ya bayar da rahoton cewa, masu adawa da muslunci a  kasar Faransa sun yi rubutu na barazanar kisan musulmi a kan bangayen masallaci a garin Cholet a unguwar Favreau.

Masu adawa da muslucni s n yi rubuce-rubuce na batun ga musulmi a kan bangayen masallacin, tare da bayyana cewa za su kashe musulmi masu salla a cikin masallacin.

Abdullahi Zikri daya daga cikin shugabannin musulmi a kasar faransa ya bayyana hakan da cewa lamari ne mai matukar hadari ga rayuwar musulmi mazauan kasar.

Y a ce yana kira ga hukumomin Faransa das u dauki mataki kan wanann lamari tun kafin lokaci ya kure.


/129